Saturday 7 February 2026 - 14:03
Juyin Juya Halin Musulunci a Iran, Ya Maye Gurbin Wulakanci da Izza da Dogaro Ga Allah

Hauza/ Limamin Juma'a na Qom ya ce: "Juyin Musulunci ya kawar da wulakanci ga jama'ar Iran, kuma ya maye gurbinsa da mutunci da kuma dogara ga Allah."

A cewar wani rahoton Ofishin Yada Labaran Hauza, Ayatullah Sayyid Hashim Hussainiy Bushahriy, a hudubar sallar juma'a ta ranar 6 ga Fabrairun 2026 wadda aka gudanar a Babban Masallacin Quds na Qom, yayin da yake magana kan cika shekaru arba'in da takwas da samun nasarar juyin Musulunci, ya ce: "Kwanaki Goma na Nasara' na juyin Musulunci ta fara ne da kyakkyawar dawowar Imam Khomeini a ranar 12 ga Bahman. A lokacin da zalunci ke mulkin kasar, an yi tarba mai girma ga Imam Marigayi. Sannan a ranar 22 ga Bahman, Imam Khomeini (RA) da nasarar juyin Musulunci, ya ba da mamaki ga kasashen Gabas da Yamma."

Limamin Juma'a na Qom ya ci gaba da cewa: "Akwai wasu halaye a cikin juyin Musulunci da suka sa aka wargaza tsarin makiyinmu. Tare da dukkan makircin da makiyinmu suka yi, mun gode wa Allah wadannan halaye sun ci gaba. Makiyinmu sun sa kasar ta dogara ga wasu, kuma sun wulakanta al'umma, dubunnan masu bada shawara 'yan Amurka su ke bada umarni, yayin da sarki na kasar bai san komai ba game da hakan."

Shugaban ƙungiyar Malamai ta Hauzar Qom ya jaddada cewa: "Juyin Musulunci ya kawar da wulakanci ga jama'ar Iran, kuma ya maye gurbinsa da mutunci da kuma dogara ga Allah. Juyin Musulunci ya shigar da mutane cikin fagen harkokin siyasa, kuma ya basu damar fahimtar yanayin siyasa. A yau, al'ummar Iran na daga cikin al'umma mafi ilimi game da harkokin siyasa, nazarin siyasa, da kuma sanin makiyi."

Limamin Juma'a na Qom ya bayyana cewa: "Makiyinmu sun gane haka, saboda haka ne ma a wasu lokuta suke hankoron 'ya'yan al'umma a cikin tarkonsu. Ba sa son Iran mai karfi."

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha